Kamfanin Dillancin Labaran Hauza ya ruwaito cewa mambobin Harkar Musulunci karkashin jagorancin Sheikh Ibraheem Yaqoub Zakzaky (H) masoya kuma mabiya gidan Manzon Allah (SAWA) a yammacin Afirka, sun sake nuna soyayyarsu da kiyaye manufofin Imam Husain (AS) ta hanyar gudanar da tarukan juyayi da zaman makoki a rana ta biyu na watan Muharram na shekarar 1448H (Yuni, 2026).
Ga takaitaccen rahoton yadda abubuwa suka wakana a sassa daban-daban na yankin:
1. Niamey (Babban Birnin Nijar); Jaddada Alkawari Kan Tabbatar da Adalci
A birnin Niamey, babban birnin Jamhuriyar Nijar, zaman juyayin Ashura na rana ta biyu ya samu halartar dimbin masu makoki a kofar gidan Sheikh Salihu Ahmad Lazaret.
A wurin taron, Sheikh Imamu Shafi'i Mamman Sharu, daya daga cikin malamai fitattu na yankin, ya gabatar da jawabi inda ya jaddada muhimmancin daukar darasi daga waki'ar Karbala: "Tsayin daka na musamman da Imam Husain (AS) yayi wajen yaki da zalunci, abin koyi ne na har abada ga kowane zamani. A yau ma, kira da tafarkin Jagora Sayyid Ibraheem Zakzaky (H) yana dauke da irin wadannan manufofi na Ashura na tsayawa kan gaskiya da neman adalci."
2. Kaduna (Nijeriya); Bayyana Tushen Tarihi na Masibar Karbala
A bangare guda a kasar Nijeriya, ginin Hussainiyyar Ahli Muhammad dake yankin Hayin Rigasa a birnin Kaduna, ya karbi bakuncin maza, mata da matasa masu juyayi da suka hallara cikin shauki.
Malam Aliyu Bakin Ruwa, Na'ibin Wakilin 'Yan Uwa na Da'irar Kaduna, shi ne babban bako mai jawabi inda ya karkata kan tushen faruwar masibar Karbala, yana cewa: "Rashin bin Wilayar da Manzon Allah (S) ya nasabta, ita ce babban mafari kuma sanadin aukuwar waki'ar Karbala da sauran masifu da suka sami al'ummar musulmi; wannan kaucewa ita ce ta ba wa gidan Umayyawa damar mamaye ragamar mulkin musulmi da juya komai don amfanin kansu."
3. Lafia (Najeriya); Gabatar da Wasan Kwaikwayo (Tamsiliyya) Na Ashura
Ita ma Da'irar Lafia a kasar Nijeriya ta shaida gudanar da gagarumin taro karkashin jawabin Sheikh Muhammad Nuraddeen Lafia mai taken "Tafiyar Imam Husain (AS) zuwa Karbala". Ya jaddada cewa duk da kokarin da makiya suka yi a tarihi na boye ta'asar Karbala, wannan fafutuka tana nan da rai, tana daukaka kuma ita ce garkuwar kare addinin Musulunci.
Daya daga cikin abubuwan da suka fi daukar hankali a taron shi ne gabatar da gajeren shiri na wasan kwaikwayo (Tamsiliyya) da matasa suka yi, wanda ke nuna yadda rundunar Yazidu ta katse wa ayarin Imam Husain (AS) hanya lokacin da suke kan hanyarsu ta zuwa Kufa, lamarin da ya taba zukatan mahalarta aka rinka zubar da kwalla.
4. Kazaure da Akure; Alakar Ashura da Nasarorin Da'irar Gwagwarmaya
Zaman juyayin Ashura a Da'irorin Kazaure (A Jihar Jigawa da ke Arewa) da Akure (A Jihar Ondo da ke Kudancin Najeriya) su ma sun sami karbuwa sosai.
A Kazaure, Malam Ahmad Ali Kazaure ya gabatar da jawabi mai taken "Tasirin Ashura da alakar nasarorin Jamhuriyar Musulunci ta Iran kan Isra'ila", inda ya bayyana cewa nasarorin da da'irar gwagwarmaya ke samu a yau a kan 'yan mulkin mallaka da sahyoniyawa, asali ne daga koyarwar shahada da sadaukarwa ta Karbala. Haka zalika, Malam Garba Hassan da Sheikh Magaji Mai Wada sun jaddada kiyaye ladubban taro da nuna juriya a tafarkin Imam Husaini.
A Akure kuwa, an gudanar da zaman karkashin jawabin Malam Salisu Muhammad kan darajar Shugaban Shahidai (AS) da kuma karanta Ziyara ta musamman ga Imam Husain (AS).
5. Potiskum (Jihar Yobe); Cigaba da Zama na Ilimantarwa a Fudiyya
Mabiya tafarkin Ahlul Baiti (AS) a birnin Potiskum na kasar Najeriya su ma sun hallara a yankin Fudiyya domin gudanar da zama na rana ta biyu. A wadannan zama na ilimantarwa, malamai sun jaddada bukatar karfafa ruhin juriya da bijire wa azzalumai, tare da raya dabi'u na mutuntaka da musulunci wadanda Imam Husain (AS) ya sadaukar da rayuwarsa dominsu.
Bisa rahoton Kamfanin Dillancin Labaran Hauza, wadannan shirye-shirye da taruka na fadakarwa wadanda ke nuna yaduwa da zurfin koyarwar Ashura a nahiyar Afirka, za su ci gaba da gudana a dukkan wadannan yankuna har zuwa rana ta goma ga watan Muharram (Ranar Ashura).
Sashin Kasashen Waje na Kamfanin Dillancin Labaran Hauza











Ra'ayinka