Talata 11 Agusta 2026 - 21:04
Shaikh Zakzaky Ya Jaddada Muhimmancin Kiyaye Fikira: “Idan Babu Jarabawa, Babu Gwagwarmaya”

Hauza/ Jagoran Harkar Musulunci a Najeriya, Shaikh Ibraheem Zakzaky (H), ya jaddada muhimmancin tunani, gane gaskiya da kuma kiyaye akidar addini a yayin rufe taron Tadrib na kwanaki uku da ƴan uwa mata na Harkar Musulunci suka gudanar a Abuja.

A cewar rahoton Kamfanin Dillancin Labaran Hauza da aka samu daga shafin Ofishin Shaikh Ibraheem Zakzaky (H), an gudanar da wannan Tadrib na kwanaki uku tare da halartar ƴan uwa mata na Harkar Musulunci, inda aka kawo ƙarshensa a ranar Lahadi, 25 ga Safar 1448, daidai da 9 ga Agusta 2026, a gidan Jagoran da ke Abuja.

A cikin jawabin da ya gabatar yayin bikin rufe Tadrib ɗin, Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) ya bayyana cewa fikira da tunani na daga cikin muhimman abubuwan da ɗan Adam yake buƙata a rayuwarsa.

Ya bayyana cewa duk da ƙoƙarin maƙiya na yaɗa gurɓatattun fikirori ta hanyoyi daban-daban domin haifar da shakku a zukatan mutane, ana iya gane gaskiya ta hanyar amfani da ma'aunin hankali da basira.

Jagoran Harkar Musulunci ya kuma yi nuni da cewa tun daga farkon kafuwar Harkar Musulunci, tushen fikira ya kasance a kan tabbatar da addini da kuma cewa addini ya kasance mai iko a rayuwar al'umma.

Ya ce maƙiya a kodayaushe suna ƙoƙarin kawar da alamomin addini domin su samu damar kawar da addini daga cikin al'umma, sai dai ya jaddada cewa irin waɗannan yunƙure-yunƙure ba su taɓa yin nasara ba, kuma ba za su iya kawo ƙarshen addini ba.

Shaikh Zakzaky ya kuma yi tsokaci kan Amurka da ƙawayenta, yana mai cewa abubuwan da ke faruwa a duniya a halin yanzu suna ƙara bayyana manufofi da ainihin shirinsu.

A cewarsa, a yau mutane da dama sun fahimci cewa zargin addini da ta'addanci da ake yi ƙarya ne, yayin da hatta waɗanda ba Musulmi ba suka fara fahimtar cewa wasu daga cikin ƙungiyoyin ta'addanci abubuwa ne da Amurka ta ƙirƙira, kamar yadda aka taɓa bayyana hakan daga ɓangaren Amurka kanta.

A ƙarshen jawabinsa, Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) ya ƙarfafa ƴan uwa da su kasance masu haƙuri da juriya, tare da kiyaye fikira da akidar addini a tafarkin gwagwarmaya. Ya ce: “Idan babu jarabawa, to babu gwagwarmaya.”

An gudanar da wannan Tadrib na kwanaki uku ne domin ƙara ilimi da wayar da kan ƴan uwa mata, da kuma ƙarfafa tushen fikira da fahimtar addini a tsakanin su.

Shaikh Zakzaky Ya Jaddada Muhimmancin Kiyaye Fikira: “Idan Babu Jarabawa, Babu Gwagwarmaya”

Shaikh Zakzaky Ya Jaddada Muhimmancin Kiyaye Fikira: “Idan Babu Jarabawa, Babu Gwagwarmaya”

Shaikh Zakzaky Ya Jaddada Muhimmancin Kiyaye Fikira: “Idan Babu Jarabawa, Babu Gwagwarmaya”

Shaikh Zakzaky Ya Jaddada Muhimmancin Kiyaye Fikira: “Idan Babu Jarabawa, Babu Gwagwarmaya”

Shaikh Zakzaky Ya Jaddada Muhimmancin Kiyaye Fikira: “Idan Babu Jarabawa, Babu Gwagwarmaya”

Shaikh Zakzaky Ya Jaddada Muhimmancin Kiyaye Fikira: “Idan Babu Jarabawa, Babu Gwagwarmaya”

Alamomi

Ra'ayinka

You are replying to: .
captcha