A cewar rahoton Kamfanin Dillancin Labaran Hauza, Shugaban ƙasar Iran, Mas’ud Pezeshkian ya gana kuma ya tattauna da Ayatullah Sayyid Mujtaba Hussaini Khamene'i, a daidai lokacin da yake fara shekara ta uku na shugabancinsa.
A yayin wannan ganawa, sun yi cikakken musayar ra’ayi kan batutuwa da matsalolin ƙasar, musamman samar da buƙatun rayuwar jama’a, yanayin da ake ciki na yaƙin tilas na uku da makomar da ke tafe, sauye-sauyen da suka shafi fagen soja, hanyoyin samar da albarkatun kuɗi da kuma yadda za a tafiyar da kashe kuɗaɗe na riyal, kuɗin waje da makamashi, da kuma hulɗar tattalin arziki da ɓangarorin ƙasashen waje.
Ra'ayinka