Jummaʼa 12 Yuni 2026 - 14:42
Mimbari Mai Daraja Shi Ne Wanda A Kansa Ake Fadar Gaskiya Da Abin Da Allah Ya Yarda Da Shi

Hausa/ Hujjatul Islam Sayyid Reza Abbas Naƙvi ya bayyana cewa darajar minbari tana tabbata ne idan a kansa ake faɗin maganar gaskiya da abin da Allah Ya yarda da shi. Ya jaddada cewa Imam Sajjad (A.S) a lokacin da aka kama shi, ta hanyar hudubobinsa ya raya saƙon Ashura kuma ya mayar da shi alamar farkawar al’umma.

Kamar yadda sashen fassara na Kamfanin Dillancin Labaran  Hauza ya ruwaito, Hujjatul Islam Reza Abbas Naƙvi, malamin addini daga Indiya, ya gabatar da wannan bayani a wani taron “Daga Ghadir zuwa Mubahala” da aka gudanar a Husainiyar Jannat‑Ma’ab a birnin Lucknow. A cikin jawabinsa ya yi bayani kan matsayin minbari a cikin addini da kuma rawar da Imam Sajjad (A.S) ya taka wajen raya saƙon Ashura, tare da jaddada muhimmancin yaɗa koyarwar Ahlulbait (A.S) a cikin al’ummar Musulmi.

Minbari a fahimtar Imam Sajjad (A.S): lokacin da sarkokin bauta suka zama sakon farkawa

Da yake magana kan matsayin huɗuba a Musulunci, ya bayyana ma’anar “minbari” yana cewa: "Minbari ba kawai itace da alluna ba ne; hakikanin minbari yana tabbata ne idan a kansa ake faɗin gaskiya da abin da Allah Ya yarda da shi."

Hujjatul Islam Reza Abbas Naƙvi ya ci gaba da cewa, kamar yadda aka ruwaito daga Imam Sajjad (A.S), Imam ɗin ya nuna wa duniya a cikin mawuyacin hali na kamu menene haƙiƙanin minbari da kuma manufar huɗubar addini, kuma ya tabbatar da cewa darajar minbari tana cikin abin da ake faɗa a kansa, ba cikin tsarin sa na zahiri ba.

Ya ƙara da cewa: "Idan a kan minbari maimakon gaskiya aka faɗi ƙarya, to wannan minbari ba komai ba ne face itace da alluna kawai kuma ba shi da wata tsarkaka. Minbari yana zama minbari ne idan a kansa ake ambaton sunan Ahlulbait (A.S) da kuma gaskiyar addinin Allah."

Wannan mai wa’azi ya kuma yi nuni da rawar tarihi da Imam Zainul Abidin (A.S) ya taka wajen raya juyin Ashura, yana cewa: "Duk da kasancewarsa cikin sarƙa da tsananin ƙuntatawa, ya isar da sakon Ashura da gaskiyar wilayar Ahlulbait (A.S) ga duniya, kuma ya girgiza ginshikan yaɗa manufofin gwamnatin Umayyawa."

Ya ci gaba da cewa: "Duk da ƙoƙarin maƙiya na daƙushe hasken gaskiya, huɗubobi da matsayar Imam Sajjad (A.S) a fadar Yazid sun bayyana haƙiƙanin zalunci da karkacewa, kuma sun raya saƙon juyin Imam Husain (A.S).

A ƙarshen wannan taro, masu jawabi da mahalarta sun jaddada ci gaba da sakon Ghadir, wilaya da Mubahala, tare da nuna muhimmancin yaɗa koyarwar Ahlulbait (A.S) a cikin al’ummar Musulmi da kuma tsakanin matasa.

Alamomi

Ra'ayinka

You are replying to: .
captcha