A cewar rahoton Kamfanin Dillancin Labaran Hauza daga shafin Ofishin Sayyid Ibraheem Zakzaky (H), a yayin ziyarar, Sheikh Muhammad Jawad Abu Qassem ya gabatar da takaitaccen jawabi, inda ya bayyana alfaharinsa da samuwar babban malami kuma jagora irin Sheikh Ibraheem Zakzaky (H), tare da jaddada muhimmancin samun mataimaka da masu goyon bayan irin wannan shaksiyya.
Ya ce: “Muna alfahari da samuwar shaksiyya mai girma ta Sheikh Zakzaky, sai dai akwai buƙatar samun mataimaka ga wannan shaksiyya, wanda ku ne waɗannan mataimaka.”
Ya kuma jaddada cewa ya kamata mahalarta tattakin Arba’in su yawaita addu’a a wannan hanya, saboda muhimmancin abin da tattakin Arba’in yake ƙunshe da shi da kuma babban matsayinsa.
A ƙarshe, Sheikh Muhammad Jawad Abu Qassem ya gabatar da addu’a domin samun tabbatuwa da dawwama, tare da yin addu’a ta musamman ga manyan malaman addini (Maraji’ai). Haka kuma ya yi addu’a ta musamman ga Jagora Sayyid Ibraheem Zakzaky (H).
An gudanar da ziyarar ne a ranar 19 ga Safar 1448H, yayin da miliyoyin masu ziyartar Imam Husaini (A.S.) ke ci gaba da tattaki daga Najaf zuwa Karbala domin gudanar da bukukuwan Arba’in.
Ra'ayinka