A cewar rahoton wakilin Kamfanin Dillancin Labaran Hauza, Ayatullah Muhammad Jawad Fazil Lankarani, memba a majalisar malaman Hauzar Qom, a gefen jerin gwano na dare da mutanen Qom suka gudanar, ya bayyana cewa: “Mun gode wa Allah, domin wannan nauyin da shugaban shahidi ya dora wa mutane, ya bayyana fiye da yadda ya ke a tunaninsa a yau.”
Shugaban Cibiyar Fiqhun A’immatul Aɗhar (AS) ya ƙara da cewa mutanen da suka nuna sadaukarwa sun tabbatar da hujja kan kowa. Daga manyan masana zuwa talakawa, sun zama hujja ga dukkan al’umman duniya. “Ya kamata a girmama waɗannan mutane saboda hankalinsu, fahimtarsu da wayewarsu.”
Fitowar mutane kan tituna ya fi darajar dubban sallolin dare
Ayatullah Lankarani ya yi nuni da cewa ko da dai an bayar da manyan shahidai a cikin wannan hanya, idan sakamakon shi ne wayewar mutane da kasancewarsu a fage, to hakan yana taimaka wa kare addini, ƙasa da daukakar da sake raya mazhabar Ahlul Baiti (AS).
Ya ce: “Abokan gaba ba su da hankali; ba su da addini, hankali ko lamiri. Ba a san da wane harshe za a yi magana da su ba. Amma duk wanda ya kalli wannan ƙasa da mutane da idon basira, zai ga faduwar ƙarfin da ake jingina wa masu girman kai, ƙarƙashin tabbatar mutanen Iran.”
Ayatullah Lankarani ya ƙara da cewa: “A yau masana harkokin soja na Amurka suna cewa tun daga Yaƙin Duniya na Biyu har zuwa yau, Amurka ba ta taɓa fuskantar irin wannan rauni daga wani ƙasa ba face Iran. Wannan shi ne ƙarfin da ɗaukakar Iran ta nuna.”
Shugaban Cibiyar Fiqhun A’immatul Aɗhar (AS) ya sake jaddada cewa fitowar mutane cikin wayo da jajircewa ya fi darajar dubban sallolin dare, kuma wannan yana da dalilai da dama. Ruwayar da ke cikin Kanz al‑Ummal daga Manzon Allah (SAWA) tana cewa: dare guda wajen tsaron Musulunci da ƙasa ya fi darajar ibada ta dare dubu, waɗanda ake azumtar ranakunsu. Saboda haka, ya ce mutane su daraja wannan fitowarsu domin wannan ma ibada ce.
Ya ƙara da cewa: "Allah Ya yi Albarka ga wannan al’umma da suke faranta ruhin shahidai. Muna fatan shugaban shahidi ya kasance cikin farin ciki a lahira ya kuma yi mana addu’a.”
A ƙarshe, Ayatullah Fazil Lankarani ya roƙi Allah Ya kiyaye shugaban juyin juya halin Musulunci, kuma Ya ba da cigaba da ƙarfi da azamar wannan juyin.
Ra'ayinka