Kamfanin Dillancin Labaran Hauza ya ruwaito cewa Ayatullah Shahid Imam Khamenei (Q) a farkon zaman darussansa na Darsul-Kharij na Fiƙhu, ya yi bayani kan wasu hadisai na ɗabi’a (Akhlaƙ). Batun yaƙini shi ne jigon wani hadisi daga Manzon Allah, Annabi Muhammad (SAWW). Ga bayanin kalamansa kamar haka:
بسم الله الرحمن الرحيم
الحمد لله ربّ العالمين
Manzon Allah (SAWA) yana daga cikin kalamansa gajeru masu hikima ya ce:
خَیرُ ما أُلقِیَ فِی القَلبْ أَلیَقین
“Khairu ma ulqiya fil‑qalb al‑yaqin.”
Ma’ana: Mafi alherin abin da Allah Madaukaki yake sanyawa a cikin zuciyar mutum shi ne yaƙini.
Idan babu yaƙini kuma shakku ya mamaye mutum, to manufofi sukan zama ba a sarari ba. Idan kuma manufa ba ta bayyana ba, tafiyar mutum ba za ta kasance madaidaiciya kuma mai ɗorewa ba. Saboda haka Allah Madaukaki ya ce game da Annabi (SAWA):
«آمَنَ الرَّسُولُ بِمَا أُنزِلَ إِلَیْهِ مِن رَّبِّهِ وَالْمُؤْمِنُونَ کُلٌّ آمَنَ بِاللهِ وَمَلآئِکَتِهِ [وَکُتُبِهِ وَرُسُلِهِ لاَ نُفَرِّقُ بَیْنَ أَحَدٍ مِّن رُّسُلِهِ وَقَالُواْ سَمِعْنَا وَأَطَعْنَا غُفْرَانَکَ رَبَّنَا وَإِلَیْکَ الْمَصِیرُ]»
Ma’ana: Manzon Allah ya yi imani da abin da aka saukar masa daga Ubangijinsa, haka ma muminai. Dukkansu sun yi imani da Allah, da mala’ikunsa, da littattafansa da manzanninsa, suna cewa ba mu bambanta tsakanin wani daga cikin manzanninsa. Suka ce: mun ji kuma mun yi biyayya; ya Ubangijinmu, muna neman gafararka, kuma zuwa gare ka ne makoma. (Suratul Baƙarah, aya ta 285)
Tafiya da hujja da yaƙini ta bambanta da tafiya da shakku da kokwanto. Saboda haka ma a cikin addu’o’i ana roƙon Allah ya ba mutum yaƙini. Ya zo a cikin wani ɓangare na addu’ar Imam Husaini (AS) a ranar Arafah:
«[اَللّهُمَّ اجْعَلْ غِنایَ فی نَفْسی] وَالْیَقینَ فی قَلْبی وَالاِْخْلاصَ فی عَمَلی وَالنُّورَ فی بَصَری وَالْبَصیرَةَ فی دینی»
Ma’ana: Ya Allah! Ka sanya yaƙini a cikin zuciyata, ka sanya tsarkakakkiyar niyya a cikin aikina, ka sanya haske a idona, da basira a addinina.
Sai tambaya ta taso: Shin yaƙini idan ya bayyana a zuciyar mutum yana nan ne har abada? Ko kuwa dole ne a kula da shi a rika ƙarfafa shi?
Amsa ita ce dole ne a rika kula da shi. Yaƙini na iya samuwa, amma wasu abubuwa da suke faruwa a rayuwar mutum ko a cikin zuciyarsa – kamar sha’awa, fushi, kwaɗayi da sauran raunin ɗabi’a – na iya raunana yaƙini kuma su haifar da shakku.
Daga cikin mummunan tasirin da zunubai suke yi shi ne lalacewar yaƙini. Allah Madaukaki ya ce:
«ثُمَّ کَانَ عَاقِبَةَ الَّذِینَ أَسَاؤُوا السُّوأَی أَن کَذَّبُوا بِآیَاتِ اللهِ [وَکَانُوا بِهَا یَسْتَهْزِؤُون]»
Ma’ana: A ƙarshe waɗanda suka aikata munanan ayyuka sun kai ga matsayin da suka ƙaryata ayoyin Allah kuma suka riƙa yi musu ba’a. (Suratur Rum, aya ta 10)
Lokacin da mutum ya riƙa aikata ayyukan da ba daidai ba saboda son zuciya da sha’awoyi, a hankali domin ya kare kansa sai ya fara lalata tushen imaninsa kamar yadda ƙwari ke cin itace har ya zama fanko.
Saboda haka mafi muhimmancin abin da Allah yake sanyawa a cikin zuciyar mutum shi ne yaƙini, kuma wajibi ne mutum ya kiyaye shi ya kuma ƙarfafa shi.
Ra'ayinka