Litinin 25 Mayu 2026 - 22:39
Rundunar Sojin Kasar Iran Ba Za Ta Taba Ja Da Baya Ba Koda Da Taku Daya Ne

Hauza/ Shugaban sashen koyar da akida da siyasa ta rundunar yan sandan Iran (FARAJA), yayin da yake magana kan karfin makaman linzami na kasar da kuma rawar da rundunonin soji ke takawa, ya bayyana cewa: "An nuna wa duniya hikimar jagora wajen bunkasa karfin makaman linzami da samar da su da yawa domin tunkarar makiya a aikace, kuma rundunonin sojin kasar ba za su taba ja da baya ba."

A cewar rahoton Kamfanin Dillancin Labaran Hauza daga Tehran, Hujjatul Islam wal Muslimin Ali Shirazi, a lokacin da yake jawabi ga taron mutanen juyin juya hali na Varamin, ya jaddada rawar da al'umma ke takawa wajen kare juyin juya halin Musulunci, inda ya ce: "Al'ummar Iran sun kasance a kowane fage na kare juyin juya hali a cikin shekaru 47 da suka gabata, kuma a yau ma sun shigo fage ne domin 'kawo karshen makiya'."

Jajircewar Al'umma da Kare Darajoji

Hujjatul Islam Ali Shirazi ya gode wa jama'a saboda kasancewarsu a fage daban-daban, yana mai cewa: "Ina godiya ga Allah da ya halicce mu a zamanin wanda ya assasa Jamhuriyar Musulunci ta Iran, Imam Khumaini (R.A), da kuma zamanin Shugaban Shuhada na juyin juya hali, Imam Khamenei (Q), da kuma a zamanin al'ummar da take kafa tarihi a kowane lokaci."

Ya kara da cewa makiya ba su fahimci wannan tsarin mai tsarki ba, ba su san darajar wannan al'umma, rundunonin soji masu karfi, da kuma ikon Wilayatul Faƙih ba. Ya ce kamar yadda al'umma suka yi nasara a yakin shekaru takwas, yau ma sun fito ne domin gamawa da makiya.

Batun Daukar Fansa da Matsayar Jagora

Dangane da tunanin makiya cewa kisan shugaban al'ummar musulmi zai kawo karshen tsarin, ya ce: "Makiya su sani cewa idan akwai abin da zai kare, to makircinsu ne zai kare, ba Jamhuriyar Musulunci ba."

Ya jaddada cewa: "Bisa umarnin Imam mai rai, Ayatullah al-Uzma Imam Sayyid Mujtaba Khamenei (H), kowane shahidi babban dalili ne na daukar fansa. Al'ummar Iran za su ci gaba da kasancewa a kan titi da kuma fagen fama har sai an aiwatar da hikimar jagora na daukar fansa ga makiya."

Karar Shari'a kan Trump da Netanyahu

Hujjatul Islam Shirazi ya bukaci a bi diddigin laifukan makiya ta hanyar shari'a: "Al'ummar Iran suna da korafi kan Trump kansa, kuma dole ne wannan korafin ya zama a hukumance. Ya kamata bangaren shari'a, ma'aikatar harkokin waje, masana shari'a na kasa, da yan sandan kasa da kasa (Interpol) su yi rajista da bin diddigin karar da jama'a suka shigar kan Trump da Netanyahu."

Karfin Makaman Linzami da Mashigar Hormuz

Shugaban sashen akida ta FARAJA ya bayyana cewa: "Idan makiya suka tsaya domin tunkarar addini, jagora, da tsarin Musulunci, al'ummar Iran za su tsaya tsayin daka wajen tunkarar dukkan masu girman kai na duniya. Idan makiya suka yi kuskure, al'ummar Iran za su kona dukkan abin da kasashen yamma suke takama da shi."

A karshen jawabinsa, ya tabo batun mashigar Hormuz, inda ya ce: "Bisa tsarin da aka sanar game da sabon tsarin tafiyar da mashigar Hormuz, al'ummar Iran da mutanen yankin ne za su yanke shawarar yadda za a gudanar da shi. Rundunonin sojin ruwa na dakarun kare juyin juya hali (Sepah) da na rundunar sojan kasa (Artesh) suna tsaye da kwarin gwiwa domin aiwatar da wannan shiri."

Alamomi

Ra'ayinka

You are replying to: .
captcha