A cewar rahoton Kamfanin Dillancin Labaran Hauza, sallar tuba ta ranakun Lahadin watan Zul‑Qa’ada ana kiranta *Aksirul A'azam* (ma’adinin magani mafi girma). Manyan malamai, ahlul‑suluk da waliyai sun nuna yin ta a duk shekara ko da a bayan Zul‑Qa’ada, tare da kawo falala da albarku masu ban mamaki.
Falalar wannan sallah
An rawaito daga Manzon Allah (SAWA) cewa duk wanda ya yi wannan salla, an karbi tubansa, an gabatar zunubansa. Zai samu albarka a gare shi da iyalansa. A ranar Kiyama, waɗanda ke da haƙƙi a kansa za su yarda da shi. Zai mutu cikin imani, kabarinsa ya faɗaɗa kuma ya haskaka. Iyayensa za su yarda da shi, su ma su shiga cikin rahamar Allah, zuriyarsa kuma a gafarta musu. Arzikinsa ya ƙaru. Mala’ikan Mutuwa kuma ya yi masa sassauci a lokacin mutuwa, ya karɓi ransa cikin sauƙi.
Yadda ake yin sallar
Manzon Allah (SAWA) ya bayyana yadda ake yin wannan salla kamar haka:
- A yi wanka a ranar Lahadi
- A yi alwala
- A yi raka’a huɗu (kowane raka’a biyu da sallama ɗaya)
A kowane raka’a:
- A karanta Suratul‑Fātiha sau 1
- Suratul‑Ikhlas (Ƙulhuwallahu) sau 3
- Suratul‑Falaƙ (Ƙul'a'uzu bi Rabbil Falaƙ) sau 1
- Suratun‑Nas (Ƙul'a'uzu bi Rabbin Nas) sau 1
Bayan salla:
- A yi istighfari sau 70
- Sai a ce:
«لا حَوْلَ وَلا قُوَّهَ اِلاَّ بِاللهِ الْعَلیِّ الْعَظیمِ»
“La haula wa la ƙuwwata illa billahil Aliyyil Azim.”
- Bayan haka a ce:
«یا عَزیزُ یا غَفّارُ، اِغْفِرْلی ذُنُوبی وَذُنُوبَ جَمیـعِ الْمُؤْمِنینَ وَالْمُؤْمِناتِ، فَاِنَّهُ لا یَغْفِرُالذُّنُوبَ اِلاَّ اَنْتَ.»
“Ya ʿAzizu ya Ghaffar, ighfir li dhunubi wa dhunuba jami'il‑mu’uminina wal‑mu’uminat, fa‑innahu l yaghfirudh‑dhunuba illa ant.”
*Tushe*: Iƙbalul A‘amal, Sayyid Ibn Dawus
*Lura:* Wannan sallah ba wai ta takaita ga ranakun Lahadin Zul‑Qa’ada kawai ba ne; ana iya yin ta a kowane lokaci domin tsarkake ruhin mutum.
Ra'ayinka