Kamfanin Dillancin Labaran Hauza-- A cewar rahoton Anadolu Agency daga jaridar Times of Israel, wani mutum ɗan shekara 36 a Kudus ya kai hari kan wata rahiba da ke aiki a makarantar Faransawa ta Littafi Mai Tsarki da koyar da tarihi a Kudus da aka mamaye. Sakamakon harin, rahibar ta samu rauni a kan gaba.
Olivier Puechion, shugaban cibiyar, ya bayyana a shafinsa na X cewa lalle wannan hari abin Allah wadai ne, kuma ba za a lamunci irin wannan ba.
Al'ummar Kirista a yankunan da Isra’ila ke mamaye su na fuskantar ire-iren waɗannan hare-hare da kuma tozarci. Baya ga haka, ana samun ƙoƙarin lalata muhimman wuraren ibada na Kirista, sata da ƙona gidaje a ɓangarori kamar Gaza, Gabashin Ƙudus, yankin West Bank da aka mamaye da kudancin Lebanon.
A ranar 30 ga watan Farvardin shekarar 1405 (19/04/2026), hotuna sun bazu a kafafen sada zumunta an nuna sojan Isra’ila yana rushe mutum-mutumin Annabi Isa (AS) da guduma a cocin da ke Deyr Serian, kudancin Lebanon. Rundunar sojin Isra’ila ta tabbatar da gaskiyar wannan hoton.
Wannan ya jaddada yadda ƙiyayya da hare-hare kan Kiristoci ke karuwa a waɗannan yankuna tare da tozarci, lalacewar dukiya, na sau da dama, da cin mutuncin mabiya addinin Kirista.
Ra'ayinka