A cewar rahoton wakilin Kamfanin Dillancin Labaran Hauza daga Isfahan, Hujjatul Islam Wal Muslimin Abdul Amir Khattat da safiyar yau, yayin ganawa da masu aikin jihadi a yankunan da aka yi wa barna a unguwar Atashgah sakamakon hare-haren ƴan ta'addan Amurkawa da Sahayoniya, ya gana da mazauna yankin. A cikin jawabinsa, tare da danganta ayar "Idan kun taimaki Allah, zai taimake ku, kuma Ya tabbatar da digadiganku", ya bayyana cewa sirrin nasara shi ne tabbatuwa. Ya ce: "Allah ya yi alƙawarin cewa idan muka tsaya a kan hanya madaidaiciya, taimakon Allah zai riske mu. Mutanenmu a cikin watanni biyu da suka gabata sun nuna basira, wayewa da dakewar zuciya."
Cika Alƙawarin Allah ga waɗanda suka sha wahala – ta baɗini da ta zahiri
Mataimakin shugaban Hauza na lardin Isfahan ya bayyana cewa: "mutane da dama daga cikin iyalai sun fuskanci asara ta baɗini da ta kudi." Ya ƙara da cewa: "In sha Allah, Allah Maɗaukaki zai cike musu waɗannan wahalhalu, kuma zai saukar da nutsuwa da albarka ga mutanen wannan yankin."
Muhimmancin Dakewar Zuciya Wajen Cimma Nasara
A wani ɓangare na jawabinsa, Hujjatul Islam Wal Muslimin Khattat ya sake komawa kan aya ta 45 cikin Suratul Anfal game da fuskantar maƙiya: «یا أَیُّهَا الَّذِینَ آمَنُوا إِذا لَقِیتُمْ فِئَةً فَاثْبُتُوا وَ اذْکُرُوا اللَّهَ کَثِیراً لَعَلَّکُمْ تُفْلِحُونَ» ya ce: bisa ga umarnin Allah, abubuwa biyu ne a matsayin mabudin nasara — tsayuwar daka da kuma yawan ambaton Allah. Don haka, a tafarkin cimma nasara da sauke nauyin Allah da kuma neman bayyanar Imam Mahdi (AJ), dole ne a yi sadaukarwa. Kamar yadda Alƙur’ani ya jaddada, tabbatuwa da ambaton Allah su ne ginshiƙan nasara.
Ya ƙara da cewa: "Yau, waɗannan ƙasashen da suke ikirarin ƙarfi sun faɗa cikin ƙasƙanci, har suna neman a tsagaita wuta. Saboda haka, da juriya da dogaro ga ikon Allah wanda ba ya ƙarewa, nasarar ƙarshe ba ta da nisa."
Godiya ta Musamman ga Mazauna Yankin da Kuma Masu Aikin Jihadi
Shugaban Cibiyar Daidaito ta Shahid Imam Khamenei ta makarantun Hauza a lardin, a ƙarshe, ya gode wa sadaukarwar waɗannan masu aikin jihadi waɗanda suka bar jin daɗinsu domin gyaran barnar da aka yi da taimakon jama’a ba tare da wani neman a biya su ba. Ya kuma nuna tarihin unguwar Atashgah a lokacin Yaƙin Kariya Mai Tsarki (Difa'e Muƙaddas), ya ce: "wannan yanki koyaushe ya kasance waje na jarumta, muƙawama da haihuwar shahidai. A yau ma, mutanen wannan unguwa, da irin wannan ruhi, suna tsaye tare da daliban Hauza da masu aikin jihadi domin taimakawa da sake gina yankin."
Ra'ayinka