Litinin 14 Satumba 2026 - 14:37
Shaikh Zakzaky Ya Gargadi Musulmi Kan Rikice-rikicen Da Maƙiya Ke Haddasawa

Hauza/ Jagoran Harkar Musulunci a Najeriya, Shaikh Ibraheem Zakzaky (H), ya jaddada muhimmancin haɗin kan al’ummar Musulmi da komawa ga sahihiyar koyarwar addinin Musulunci, yana mai cewa maƙiya suna amfani da rikice-rikice da rashin haɗin kan Musulmi wajen cimma manufofinsu.

A cewar rahoton Kamfanin Dillancin Labaran Hauza, Sheikh Ibraheem Zakzaky (H) ya bayyana hakan ne a yayin da yake gabatar da jawabi a taron Mauludin Manzon Rahma (S), wanda Dandalin Resource Forum na Harkar Musulunci ya shirya a ranar Lahadi, 13 ga Satumba 2026, daidai da 1 ga Rabi’ul Thani 1448.

Jagoran Harkar Musulunci ya tunatar da mahalarta muhimmancin komawa ga koyarwar Manzon Rahma (S), yana mai cewa: “Manzon nan ya zo da addini kammalalle, cikakke, kuma ya ɗora al’umma a kai. Abin da ya hau kanmu shi ne mu bi.”

Ya bayyana cewa maƙiya suna ƙoƙarin aibata matsayin Manzon Rahma (S), saboda sun fahimci cewa Musulmi suna kallonsa a matsayin wata babbar alama da ke haɗa su.

A wani ɓangare na jawabinsa, Shaikh Zakzaky ya ja hankalin al’ummar Musulmi kan rikice-rikicen da ake haddasawa a tsakaninsu, yana mai cewa rikicin da ake haifarwa da sunan addini ko ƙabilanci ba zai amfanar da al’ummar Musulmi ba, sai dai ya amfani maƙiyan da ke haddasa irin waɗannan rikice-rikice domin biyan buƙatunsu.

Ya ƙara da cewa ana haddasa rikice-rikice da matsalolin tsaro ne domin ɗauke hankalin jama’a daga muhimman al’amuransu, yayin da ake ci gaba da wawure dukiyoyinsu tare da ƙara jefa mutane cikin talauci da rarrabuwa.

Jagoran Harkar Musulunci ya bayyana cewa fahimtar dabarun maƙiya, haɗin kan al’umma da komawa ga sahihiyar koyarwar Manzon Rahma (S) su ne hanyoyin da za su taimaka wajen samun mafita daga matsalolin da al’ummar Musulmi ke fuskanta.

Taron Mauludin, wanda Dandalin Resource Forum ke shirya wa duk shekara, ya samu halartar mutane daga sassa daban-daban na al’ummar Musulmi, ciki har da limamai, malamai, ma’aikata da sauran jama’a.

Shaikh Zakzaky Ya Gargadi Musulmi Kan Rikice-rikicen Da Maƙiya Ke Haddasawa

Shaikh Zakzaky Ya Gargadi Musulmi Kan Rikice-rikicen Da Maƙiya Ke Haddasawa

Shaikh Zakzaky Ya Gargadi Musulmi Kan Rikice-rikicen Da Maƙiya Ke Haddasawa

Shaikh Zakzaky Ya Gargadi Musulmi Kan Rikice-rikicen Da Maƙiya Ke Haddasawa

Shaikh Zakzaky Ya Gargadi Musulmi Kan Rikice-rikicen Da Maƙiya Ke Haddasawa

Shaikh Zakzaky Ya Gargadi Musulmi Kan Rikice-rikicen Da Maƙiya Ke Haddasawa

Shaikh Zakzaky Ya Gargadi Musulmi Kan Rikice-rikicen Da Maƙiya Ke Haddasawa

Alamomi

Ra'ayinka

You are replying to: .
captcha