A cewar rahoton Kamfanin Dillancin Labaran Hauza, Ayatullah Alamul-Huda ya bayyana haka ne a wajen taron tunawa da arba’in din Shahidin Jagora da kuma fara sabuwar shekarar karatu ta Makarantar Fiƙhun A’imma (A.S), inda ya ce: "makomar Hauzar ilimin Khurasan na da kyakkyawan fata wajen gina wayewar Musulunci, kuma Hauzar na da damar samar da malamai masu ilimi, zamani da ƙwarewa domin hidima ga Hazrat Baƙiyyatullah (A.S).
Yayin da yake bayanin labarin halifancin Annabi Adam (A.S), ya bambanta tsakanin ilimi da “Anbaa”, yana mai cewa samun ilimi kaɗai bai isa ya mayar da mutum mai gina al’umma ba; a maimakon haka, dole ne ilimi ya koma zuwa bayani, wa’azi da tasiri a cikin al’umma.
Wakilin Waliyyul Faƙih a Khurasan Razavi ya ƙara da cewa ya kamata Hauzozin ilimi su ƙarfafa ikon ɗalibai wajen wa’azi, bayyana gaskiya da yin tasiri a cikin al’umma, domin mutum na iya samun ilimi mai yawa amma idan ba shi da ikon isar da shi da yin tasiri, ba zai iya taka rawar da ta dace a cikin al’umma ba.
Ayatullah Alamul-Huda ya jaddada cewa ɗalibin Hauza bai kamata tun daga farkon shigarsa ya sa burinsa ya zama samun mukamai kamar alƙalanci, shugabanci ko wasu matsayi na zamantakewa ba. Maimakon haka, ya kamata ya shiga Hauza da niyyar hidima ga Imam Mahdi (A.S), ya kuma yi amfani da dukkan ƙarfinsa na ilimi da aiki wajen wannan manufa.
Ya kuma yi nuni da rawar da Imam Hadi (A.S) da Imam Hassan Askari (A.S) suka taka wajen shirya mabiya Shi’a domin zamanin gaibar Imam Mahdi (A.J), yana cewa waɗannan Imamai biyu sun aza tubalin tsarin fiƙihu, marja’iyya da tsarin malamai, domin Shi’a su iya tafiyar da rayuwarsu ta addini a zamanin gaibar Imam kai tsaye, bisa koyarwar Ahlul-Baiti (A.S).
Wakilin Waliyyul Faƙih a Khurasan Razavi ya kammala da yin nuni da irin zalunci da shahadar Imam Hasan Askari (A.S), yana jaddada muhimmancin ci gaba da tafarkin da Imam ya kafa, tare da yin addu’ar gaggauta bayyanar Imam Mahdi (A.S) da samun nasarar Hauzozin ilimi wajen hidima ga addini da al’ummar Musulmi.
Ra'ayinka