A cewar rahoton Kamfanin Dillancin Labaran Hauza, Shugaban Makarantun Hauzar Iran, Ayatullah Alireza A'arafi ya bayyana cewa, babban aikin Hauza shi ne zurfafa ilimin addini, musamman Fikihu da Usul, tare da ci gaba da kiyaye gadon ilimi na sama da shekaru dubu, yayin da ake samar da amsoshi ga sabbin buƙatun al’umma da sauye-sauyen duniya.
Ya kuma jaddada cewa Jamhuriyar Musulunci ta Iran a shirye take ta fuskanci barazana da sauye-sauye, yana mai cewa Hauza tana tare da al’ummar Iran kuma tana bin jagorancin manyan maraji'ai da tsarin Wilayatul Faƙih.
Ayatullah A'arafi ya buƙaci a yi amfani da darussa na tarbiyya, ɗabi’a, sadaukarwa da juriya da aka samu daga yaƙi wajen tarbiyyar ɗaliban Hauza da sauran al’umma, musamman matasa, ɗalibai da ɗaliban jami’a.
Ya kuma jaddada muhimmancin ƙarfafa matsayin Marja’iyya da Wilayatul Faƙih, tare da tabbatar da cewa sabbin ɗalibai da malamai sun fahimci tunani da koyarwar Imam Khumaini da sauran manyan jagororin juyin juya halin Musulunci.
A fannin wa’azi da wayar da kai, Ayatullah A'arafi ya bayyana Jihadin Bayyanawa (Jihadut-Tabyin) a matsayin muhimmin nauyi na kullum ga Hauza, musamman wajen gabatar da bayanai sahihai da amsa shubuhohi da tambayoyin al’umma.
Ya ce ƙarfin ilimi, na Fikihu da na tunani shi ne ginshiƙin aikin Hauza, amma ya kamata a haɗa shi da ƙarfin ruhi, na tarbiyya da kyawawan ɗabi’u domin samar da malamai masu ilimi da kuma nagartaccen hali.
Ayatullah A'arafi ya kuma yi kira ga malamai da ɗalibai da su ƙara kusanci da al’umma, musamman matasa, ɗaliban makarantu da jami’o’i, tare da kasancewar Hauza mai jagoranci, mai tasiri, mai kuzari kuma mai iya amsa buƙatun al’umma.
A bangaren fasaha, ya jaddada amfani da sabbin fasahohi, ciki har da fasahohin zamani, wajen inganta ilimi, bincike, wa’azi da sadarwa, amma ya ce hakan dole ne ya kasance tare da kiyaye ingantattun tushe da hanyoyin ijtihadi na Hauza.
A ƙarshe, Ayatullah A'arafi ya yi kira ga malamai, makarantu da cibiyoyin Hauza da su ba da fifiko ga ilimi, bincike, hulɗa da jama’a, tarbiyyar ɗalibai da ayyukan wa’azi, yana mai fatan cewa za su ci gaba da hidimtawa Musulunci da al’umma cikin basira, ilimi, ɗabi’a da himma.
Ra'ayinka