A cewar rahoton Kamfanin Dillancin Labaran Hauza, a ranar Juma'a 10 ga Yulin 2026, Sheikh Ibraheem Zakzaky (H) ya karɓi baƙuncin wasu maziyarta daga Birtaniya a masaukinsa da ke birnin Mashhad Mai Tsarki. Waɗannan maziyartan sun zo Jamhuriyar Musulunci ta Iran ne domin halartar jana'iza da kuma taron girmama Shahid Ayatullah Sayyid Ali Husaini Khamene'i (QS).
A cikin jawabinsa ga baƙin, Shaikh Zakzaky (H) ya ce: "Ku kasance jakadu nagari, ku kuma isar da ingantaccen saƙo da asalin addinin Musulunci ga mutane."
Ya kuma jaddada cewa nauyi ne da ya rataya a wuyan Musulmi su bayyana hakikanin fuskar Musulunci ga duniya, tare da ƙara himma wajen yaɗa ƙimomin Ubangiji, haɗin kan Musulmi, da kuma isar da saƙon adalci, ruhaniya da gwagwarmaya ga al'ummomin duniya.
An gudanar da wannan ganawa cikin yanayi na ƙauna da ruhaniya. Mahalarta taron sun kuma bayyana alhininsu ga al'ummar Iran kan shahadar Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci, tare da jaddada ci gaba da tafarkin shahidai da kuma yaɗa Musulunci na Asali na Annabi Muhammad (SAWA) ga duniya baki ɗaya.




Ra'ayinka