A cewar rahoton Kamfanin Dillancin Labaran Hauza, tawagogin makoki daga yankuna daban-daban na birnin Qum, tare da wasu daga biranen Zanjan, Arak da Gabashin Azerbaijan, sun halarci bukukuwan Ashura a haramin cikin tsari da ladabi. Haka kuma, tawagogi daga ƙasashen Iraki, Afghanistan, Pakistan da wasu sassan Afirka da suka haɗa da mabiyan Sheikh Ibraheem Zakzaky (H) sun kasance cikin mahalarta wannan gagarumin taro na addini.
Rahoton ya nuna cewa haɗin gwiwar masu hidimar harami, jami’an tsaro da ƙungiyoyin agaji ya taka muhimmiyar rawa wajen samar da yanayi mai aminci da natsuwa ga dubban masu juyayi da suka halarci bukukuwan.
Masu lura da al’amura sun bayyana cewa wannan taro ya sake nuna matsayin birnin Qum a matsayin ɗaya daga cikin muhimman cibiyoyin ilimin Ahlulbait (A.S.) da kuma wajen haɗuwar masu kaunar Imam Husaini (A.S.) daga ƙasashe da al’ummomi daban-daban.
A cewar rahoton, halartar tawagogin ƙasashen waje ya nuna cewa saƙon Ashura bai takaitu ga wata ƙasa ko al’umma guda ba, sai dai saƙo ne na duniya wanda ke haɗa al’ummomi a kan ginshiƙan adalci, juriya da biyayya ga gaskiya.
Taron Ashurar bana a Qum ya gudana cikin tsari mai kyau, inda masu juyayi suka gudanar da salla, karatun addu’o’i, waƙoƙin makoki da sauran ibadodi a cikin yanayi na girmamawa da ruhi.







Ra'ayinka