Kamfanin Dillancin Labaran Hauza ya ruwaito cewa: Shahidin Jagoranmu mutum ne mai fannonin basira da yawa, kuma muhimmin mabuɗin fahimtar shi “rayuwar sa ta Alƙur’ani” ce. Ya tashi da Alƙur’ani, ya saba da shi, kuma tunaninsa, motsinsa, ɗabi’unsa da hatta salon jagorancinsa duk daga Alƙur’ani suke fitowa. A wurinsa, Alƙur’ani ba kawai littafin karatu ba ne, amma wata babbar ma’ajiyar Ubangiji ce da taswirar fahimtar fikihu, tarihi, al’ummomi, tarihin annabawa, makomar duniya da ƙarshen tafiyar ɗan Adam. Saboda haka, shi kansa malamin tafsirin Alƙur’ani ne kuma masani ne a tarihin Annabi (SAWA) da A'imma (AS), yana kuma yarda cewa ba za a fahimci Alƙur’ani daidai ba tare da Annabi da magadansa ma’asumai ba.
Daya daga cikin fitattun siffofinsa shi ne tsarin jagorancin sa na Alƙur’ani wanda ya samo asali daga rayuwar Ma'asumai goma sha hudu (AS); abin da ake iya ganin taƙaitaccen bayyanuwarsa a cikin littafin “Mutum mai Shekara 250”. Ta hanyar zurfin nazari da sakamakon bincike kan rayuwar Annabi (SAWA), Sayyida Zahra (AS) da Imamai goma sha biyu (AS), ya tara babban tarin ka’idoji na jagoranci, siyasa da zamantakewa, kuma yana amfani da su a aikace. Daya daga cikin jaddadawarsa ita ce mahimmancin bin sirrin siyasar A'imma (AS), wato gano dabarun da suka yi amfani da su a kowane zamani da irin matakan da suka ɗauka.
Domin karin fahimtar wannan Faƙihi na gari kuma jagoran shahidai, mun tattauna da Hujjatul Islam Wal Muslimin Asgar Dairbaz, mamba a Majalisar Zaɓen Jagora (Majalise Khubregan) kuma malami a Hauzar Ilimi ta Qom, a kasa ga cikakken bayanin tattaunawar:
Tambaya: Dangane da siffofi da halayya da tsarin gudanarwar Shahidin jagoranmu, la’akari da cewa kun yi zama tare da shi, kun yi da mu’amala da shi, kuma kuna da sanin dangane da shi tsawon shekaru da dama—wadanne abubuwa ne suka fi tasiri a zukatanku da kuke son haskakawa ga masu karatunmu?
Amsa: Akwai bayanai masu yawa game da girman halayen Shahidin jagoranmu. Amma bisa iyakar fahimtata, da kuma lokacin da muke da shi, zan ambaci wasu muhimman al’amura. Wataƙila mafi muhimmanci a ganina shi ne: manyan malamai a Hauza ko jami’o’i, galibi kowannensu na iya zama ƙwararre a fanni ɗaya ko biyu; ɗaya zai kasance babban masani a fikihu, wani a falsafa, wani kuma masanin tafsiri a wani fanni na musamman.
Amma idan za mu nemi kalmar da ta fi dacewa wajen bayyana halayen Shahidin jagoranmu, za mu iya cewa: mutum ne mai halayen Alƙur’ani. Wato ya tashi da Alƙur’ani, ya saba da shi, kuma tunaninsa, halayensa, motsinsa da dukkan ɗabi’un sa daga Alƙur’ani suke samo asali.
A cikin Alƙur’ani akwai fikihu; akwai tafsiri; akwai ayoyin ahkam (hukunce-hukunce); akwai ka’idojin istinbaɗ da za a iya samo su; akwai tarihin al’ummomi da suka gabata; akwai bayanai kan wayewar da ta gabata kafin Musulunci; akwai tarihin Annabawa; akwai manyan batutuwa kan akida, makomar duniya da ƙarshen tafiyar ɗan Adam.
Mutum mai halayen Alƙur’ani, tare da jagoranci da ya dace da Alƙur’ani
Alƙur’ani wani babbar ma’ajiyar Ubangiji ce, wata taswira ce da ke bayyana nufin Allah Madaukakin Sarki. Don haka, jagoranmu wanda yake da halayen Alƙur’ani, ya kasance malamin tafsiri. Bugu da ƙari, ya kasance mai zurfin sani kan tarihi. Alƙur’ani ba zai bada cikakken ma’ana ba tare da Annabi (SAWA) ba; rayuwar Annabi, sirarsa, da rayuwar wasiyyansa – waɗanda muke kira Imamai goma sha biyu – su ne cikakkiyar ma’anar fahimtar Alƙur’ani.
Wadannan Imamai su ne wasiyyan Annabi, waɗanda Allah Ya naɗa, kuma Annabi ne ya gabatar da su. Ma’anar wannan tsokaci ita ce: babban mabuɗin fahimtar halayen Shahidin jagoranmu shi ne cewa shi shaksiyyar Alƙur’ani; motsinsa Alƙur’ani ne, tunaninsa Alƙur’ani ne, kuma jagorancinsa ma daga Alƙur’ani yake.
Game da jagorancinsa kuwa, za mu iya cewa: akwai shugabanni da yawa da su kansu masu ƙoƙari ne, masu aiki, kuma suna da kyakkyawan sakamako, amma basu da ƙwarewar tara mutane da tura su kan hanya guda domin cimma manufofin su. Shugaba kuwa, banda zurfin tunani, hangen nesa, ƙwarewar tsarawa, sa ido, da gina tsari – waɗanda ake ambata a ilimin gudanarwa – dole ne ya mallaki iya haɗa ƙwararru da jama’a domin su yi aiki bisa manufarsa.
Jagora wanda yake gano mutane kuma ya tara ƙarfinsu domin hidimar juyin juya hali
A wannan fanni, Shahidin jagoranmu yana da irin wannan fasaha sosai. Da farko yana da kwarewar gane mutane daidai; yana lura da halaye, motsi da matsayinsu a cikin al’umma, yana kuma bibiyar su a kowane lokaci. Ta haka yake samun cikakkiyar fahimta game da kowanne mutum, sannan kuma yana amfani da ƙarfinsu wajen ci gaban manufofin juyin juya hali. Wannan ɗaya daga cikin manyan ƙwarewarsa ce a fannin gudanarwa.
Wata ƙwarewarsa a shugabanci ita ce: ba ya takaita kansa da abin da ya gada daga wasu. Sau da yawa masu jagoranci suna bin hanyar da aka bari a baya ba tare da ƙara wani abu ba, amma shi yana mai da hankali kan sabbin tunani, sabbin ka’idoji da kirkire‑kirkire a jagoranci. A gaskiya, fasahar jagoranci tana ɓoye a cikin kirkire‑kirkire, domin a tafiyar gudanarwa, yanayi da matsaloli masu sabo sukan bayyana, kuma wani lokaci wajibi ne a samar da mafita mafi dacewa cikin gajeren lokaci. Wannan kuma sai idan shugaba yana da ikon kirkira, ba wai kawai dogaro da abin da aka gada daga wasu ba—kodayake waɗancan ma’auni na iya amfani—amma dole ne a haɗa su da kirkira.
Littafin “Mutum mai Shekara Dari Biyu Da Hamsin (250)” a matsayin taƙaitaccen hangen sirar A'imma (AS)
Abu na uku da zan iya cewa shi ne: saboda sabgarsa da zurfin aikinsa kan rayuwar Manzon Allah (SAWA), Sayyida Zahra (AS) da Imamai ma’asumai (AS), idan muka nemi misalin jagoranci na Musulunci a aikace, za mu same shi a cikin sirar su: daga Annabi (SAWA), Amirul Muminin (AS), Imam Hassan (AS), Imam Hussain (AS), Sayyida Zahra (AS), har zuwa Imami na goma sha biyu (AJ). Daya daga cikin muhimman ayyukan da Shahidin jagoranmu ya sadaukar da rayuwarsa a kai shi ne nazari mai zurfi da ci gaba kan sirar Manzon Allah (SAWA), Sayyida Zahra (AS) da sauran A'imma (AS).
Littafin “Mutum mai Shekara 250” ana iya kiran sa taƙaitaccen sakamakon wannan aiki. Mutumin da yake da zurfin sani a dukkan matakan rayuwar Annabi (SAWA) – kafin hijra, bayan hijra, yaƙe‑yaƙe, harkokin iyali, hanyarsa ta tarbiyya, dangantakar kasashen waje, halaye da juriyarsa – sannan ya bi sirar Amirul Muminin da sauran Imamai, a lokacin da ba su da jagoranci kai tsaye da kuma a lokacin da suke da shi, kuma ya bi duk sirar ma’asumai goma sha huɗu, tabbas zai gane cewa al’umma koyaushe tana cikin sauyi. Don haka mai gudanar da al’umma dole ne ya mallaki ƙarfin jagoranci da ya dace da kowanne sabon yanayi.
Hankalin Shahidin jagoranmu ya kasance kan sira ta siyasar A'imma (AS)
Duk wanda ya yi zurfin nazari da nazarin sigogi a sirar ma’asumai, musamman da irin hangen da Shahidin jagoranmu yake da shi, zai iya tara manyan ka’idoji daga wannan taska. Wasu mutane suna mai da hankali ne kawai kan sirar akhlaƙ, wanda tabbas yana da muhimmanci; wasu kuma kan sirar iyali, ibada ko tattalin arziki. Amma Shahidin jagoranmu musamman yana mai da hankali kan sira ta siyasa—wato: a wane yanayi Annabi (SAWA), Sayyida Zahra (AS) da Imamai goma sha biyu (AS) sun ɗauki wane matsayi? Wane dabaru suka yi amfani da su? Wane matakan siyasa suka aiwatar?
Wanda ya binciki wannan tarihin shekaru 250 da zurfin tunani zai iya fitar da ka’idoji masu yawa na jagoranci da gudanarwa. Don haka, a kowane lokaci da kuma a kowane yanayi, za a iya samun hanyar jagoranci daga sirar A'imma. Shahidin jagoranmu ya kasance yana amfani da wannan taska na ilimi daidai gwargwado, kuma akwai misalai da shaidu da yawa a kan hakan.
Tsayuwa cikin jarumta koyaushe a gaban zalunci da danniya
Wata siffa da za a iya ambato game da shi ita ce: idan aka kalli sirar Manzon Allah (SAWA) da A'imma (AS), za a ga a sarari cewa ɗaya daga cikin siffofinsa mafi fitowa fili shi ne tsayuwa cikin jarumta, ba tare da kasala ba, a gaban zalunci, danniya da girman‑kai — har zuwa ƙarshe.
Akwai mutane da za su yi gwagwarmaya a wani lokaci na rayuwarsu, daga baya kuma saboda tsufa ko dalilai daban-daban su ja da baya. Wasu kuma suna iya nuna jarumta a wasu lokuta amma daga baya su rasa wannan ruhin. Amma wanda ya ci gaba da gwagwarmaya har zuwa ƙarshe tare da jarumta, kuma ya iya tsayawa gaban ɓata har ya kayar da shi — wannan shi ne abin da ake kira fitacciyar siffar jagoranci.
Sau da dama an ji cewa makiya Musulunci da masu girman‑kai na duniya suna tsara dabaru da makirce‑makirce, amma Shahidin jagoranmu, ta hanyar jawabi guda ko matsaya guda daidai, yana rushe dukkan shirin su. A cikin gida ma, an sha fuskantar makircin ciki iri‑iri, amma shi, ta hanyar ganewa da wuri, sanin wane matsayi ya dace a wane lokaci, me za a faɗa da yadda za a gudanar, yana lalata dukkan waɗannan makirce-makircen. Ma’ana shi ne: ruhin adawa da danniya da tsayuwa a wannan hanya ya kasance a cikinsa koyaushe — kuma a wannan hanya ya samu shahada.
Shiga kai tsaye cikin wasu lamurra masu muhimmanci
Wani abu kuma shi ne: a wasu lokuta, saboda muhimmancin lamari, Shahidin jagoranmu da kansa ya jagoranta kai tsaye. Wannan jagoranci ne na filin aiki — a tsakiyar al’amari.
Zan kawo misalai biyu.
Na farko: abubuwan da suka faru a shekara ta 1388 (2009). A wancan lokaci, jam’iyyu da kungiyoyi daban-daban sun shiga filin da furuci iri‑iri, kuma kowa yana da abin da yake tsammani daga Jagora. Shahidin jagoranmu ya tara duk shugabanni da waɗanda suke da ƙorafi ko matsayi. A cikin taron da aka yi, ya bayyana a sarari cewa: “Ni ne mai gudanar da wannan zama kuma ni da kaina zan jagorance shi.” Haka kuwa ya yi. Ya saurari maganganunsu, ya ba da amsoshi, ya bayyana mafita. A wasu wurare kuma ya bayyana kai tsaye cewa wasu shawarwari ba daidai ba ne — kamar maganar kawo tawagar ƙasar waje domin tantance sahihancin zaɓen kasar. Ya bayyana cewa wannan ra’ayi ba daidai ba ne, domin Jamhuriyar Musulunci da kanta tana da hukumomin sa ido masu ƙarfi da inganci, kuma babu bukatar wani ƙasashen waje. A dukkan waɗannan, ya tsaya da hujja mai ƙarfi, da ƙwaƙƙwarar magana, kuma cikin gamsarwa.
Shahidin Jagora ba ya magana da ɗalibai daga matsayin iko ko umarni
Misali na biyu: ganawarsa da ɗalibai. Sau da yawa wadannan ganawa suna ɗaukar sa’o’i biyu zuwa uku. Dalibi kuwa, musamman matashi, yana son yin tambaya, sukar abin da ya gani ba daidai ba, kuma yana kallon kansa a matsayin mai neman gaskiya. Shahidin jagoranmu yana sauraron su da hankali. Idan sukar su gaskiya ce, yana karɓa; idan kuma akwai buƙatar bayani, yana yi da cikakken haske.
Wani ɗalibi na iya fita daga taron yana da shakku ko rashin yarda da wasu maganganunsa, amma muhimmin abu shi ne: shi ba ya yin magana daga matsayin iko, irin tamkar “Ni shugaba ne kuma dole ne ku yi biyayya.” A’a — maganarsa bisa hujja ce, tausayi, dalili, da nufin gamsarwa. Wannan ɗaya daga cikin fitattun siffofin jagorancinsa ne.
Wani misali kuma shi ne rawar da ya taka a cikin yaƙin kwanaki goma sha biyu. A lokacin ma da kansa ya shiga filin ya jagoranci aikin daga gaba. Wannan ma wata alama ce ta jagorancinsa a filin aiki.
Tsayuwarsa kan tsarin da ya yarda da shi, duk da cewa yana yarda a yi nazari, a yi gyara, ko ma a yi sassauci a lokuta na musamman — amma yana jaddada cewa irin waɗannan canje‑canje sai an tattauna su da ƙwararru, ba a yanke su nan take a gaban taro ba.
Jaddawalin da yake yi koyaushe wajen bin diddigin al'amurra da ayyuka
Abu na ƙarshe da zan so in ambata — kuma zan yi ƙoƙarin kada ya ɗauki lokaci — shi ne batun bin diddigi a cikin jagoranci. Sau da yawa an ambata cewa duk shekara, a lokacin kwanaki takwas na Shahrevar (a lokacin tunawa da shahadar Shahid Raja’i da Bahonar) kuma a makon gwamnati, ministocin gwamnatoci daban‑daban suna zuwa gaban Shahidin jagoranmu.
Baya ga cewa a waɗannan taruka yana gabatar da nazari mai zurfi game da yanayin ƙasar, yana kuma bayar da wasu shawarwari. Idan aka duba shawarwarin da ya bayar ga gwamnatoci tsawon shekaru ashirin — misali a ɗauka cewa a kowane zama shawarwari goma aka faɗa — sannan a binciki wanne daga cikinsu ya maimaita da wanne bai maimaita ba, za a ga cewa wasu daga cikin wadannan shawarwari an maimaita su. Wannan maimaitawar tana nuna cewa batun bai warware gaba ɗaya ba; watakila gwamnati ta ɗan yi aiki a kansa amma ko dai an yi rauni ko kuma aikin bai kai ƙarshe ba, saboda haka shi ya ga wajibi a sake tunatarwa da bin diddigi. Ba ya dogara da mantuwa irin na cewa “sau biyu ko uku na faɗa, ya isa,” a’a, yana ganin cewa dole ne a bi abu har sai an ga sakamakon da ake nema.
Ɗaya daga manyan dabarun gudanarwa kuwa shi ne wannan bin diddigi. Shahidin jagoranmu sau da yawa ya faɗa a sarari cewa idan wani mai gudanarwa yana da halin bin diddigi, kashi casa'in na nasara tana kusa da tabbata. Amma shugaba wanda ya bada umarni sau ɗaya sannan ya manta da shi saboda ayyuka masu yawa, ba zai iya tsammanin cikawar al’amura ba; domin ma’aikata ma ba za su bi al’amarin sosai ba, don haka lamari zai tsaya a tsakiyar hanya har sai wata rana shugabanni sun tuna da cewa sun taba bayar da irin wannan umarni.
Shahidin jagoranmu ba shi da irin wannan hali. Sau da dama yana iya cewa: “Na bada umarni a kan wannan amma bai cika ba,” alhali kuwa shi kansa ya riga ya bi diddigi, sai dai saboda wasu matsaloli ko yanayi na musamman aikin bai kai ƙarshe ba.
Abin da nake nufi shi ne: idan za mu rubuta littafi game da tsarin gudanarwar Jagora, za a iya rubuta littattafai da dama. Wani aboki yana ba da labari cewa a game da ra’ayoyin Shahidin jagoranmu kan Imam Mahdi (AJ) da batun Mahdawiyya ya tattara kusan shafuka ɗari shida na bayanai — bayanan da suke kunshe da dukkan bayanan sa game da bangarori daban‑daban na Imamuz Zaman (AJ), bayyanarsa da batun Mahdawiyya.
Wannan yana nuna cewa a kowane fanni, ciki har da shugabanci, ya kasance da tsari da tunani mai zurfi kuma mai haɗin kai, wanda ake iya nazarinsa. Litattafai da rubuce‑rubuce ma an yi su game da salon jagorancinsa. Abin da nake son in ce shi ne: muna gaban mutum ne wanda ba kasafai ake samun irinsa ba, mutum ne na musamman. Duk da cewa rashin sa babban rashi ne, kuma jininsa ya haifar da farkawa da motsi a cikin al’umma, amma har yanzu akwai fannoni da yawa na halayensa da ba a yi musu bayani sosai ba, waɗanda ake buƙatar lokaci da zarafi domin tattaunawa a kansu.
Tambaya da amsa game da yadda aka zaɓi jagora na uku na juyin juya halin Musulunci
Tambaya: Tunda kai ɗaya ne daga mambobin Majalisar Khubregan (Majalisar Zaɓen Jagora), masu karatunmu da yawa suna son jin bayanai daga bakinku game da yadda aka zaɓi Jagoran Juyin Juya Halin na Uku, Ayatullah Sayyid Mujtaba Hussaini Khamenei. Wasu daga cikin mambobin majalisar sun riga sun yi bayanai a baya. Idan akwai wani muhimmin abu daga wannan zama ko hanyar zaɓen, muna sauraro.
A wannan batu, ina so in ambaci abubuwa biyu da nake ganin suna da muhimmanci.
Abu na farko shi ne: Majalisar Khubregan ta yi nazari da tsantseni sosai wajen tantancewa ko siffofi da sharuddan da Kundin Tsarin Mulki ya ayyana domin matsayin jagoranci suna samuwa, da a wane mataki suke akwai, cikin wadanda ake ganin suna da cancanta. Wannan tantancewar kuwa an yi ta ne daki-daki, ta fuskar mutum ɗaya-bayan-ɗaya da kuma ta fuskar gungun shawarwari. Lallai an yi aiki da cikakken taka-tsantsan, da zurfin tunani, ba tare da wani sakaci ko rangwame ba — ganin girman matsayin jagoranci a cikin al’ummar Musulunci da ma duniya.
Abu na biyu, wanda nake ganin yana da matuƙar muhimmanci, shi ne: kamar yadda zukatan mutane da dama suka samu soyayya da sanin darajar Ayatullah Sayyid Mujtaba Hussaini Khamenei — duk da cewa da yawa ba su taɓa ganin shi ko jin maganarsa ba — haka ma mambobin majalisar. Wato tare da binciken sharuddan jagoranci, zuciyoyinsu ma sun samu soyayya da ma’arifa gare shi. Wannan alheri ne daga Imamuz Zaman (AJ), wanda ya sanya wannan ƙauna da ma’arifa a zukatan mutane da ma na mambobin majalisar.
Wannan ba ya sabawa amfani da hankali, bincike da ƙwarewar masana. Yana da halin sa cewa zukata su shiga tunani, a tattauna hanyoyin aiki. Ni na kasance a Majalisar Khubregan a zaman ta na huɗu da na biyar, kuma yanzu a na shida. A zaman ta na biyar, ɗaya daga cikin mambobi ya yi jawabi na ɗan lokaci game da halayen Ayatullah Sayyid Mujtaba Hussaini Khamenei, sauran kuwa suka saurara cikin nutsuwa ba tare da wata magana — ba amincewa, ba adawa. Domin a lokacin, kowa yana addu’a ne Allah ya tsawaita rayuwar Shahidin Jagoran, domin ya mika tutar juyin juya hali ga Imamuz Zaman (AJ) don bayyanar sa ta yi sauri.
Sanya soyayya cikin zukata da yardar Imamuz Zaman (AJ)
A irin wannan yanayi, mutane ba sa yin tunanin maganar wanda zai gaje shi sosai — kodayake kowa ya san cewa wata rana lamarin zai faru. Shahidin jagoranmu ma a wasu lokuta yana tunatarwa cewa wannan shi ne babban aikin majalisar.
Saboda haka, tare da tsantseni da natsuwar da aka yi wajen daidaita siffofi da sharuddan jagoranci, soyayya da ma’arifar da aka sanya a zukata game da Ayatullah Sayyid Mujtaba Hussaini Khamenei ta taimaka wajen kafa ra’ayin mafi yawan mambobin. Ni ban ga wani karin bayani dangane da wannan hadin kai ba face wannan gaskiya.
Akwai wasu da aka tattauna kansu amma ba zan ambaci sunaye ba; su ma mutane ne manya da kwararru. Amma Majalisar Khubregan, bisa ganin inganci a fannoni irin su halayya, fikihu, ijtihadi da shugabanci, ta zaɓi Ayatullah Sayyid Mujtaba Hussaini Khamenei. Kashi mafi rinjaye sun tsaya a wannan ra’ayi. Duk kuwa da cewa wasu mutane sun yi ƙoƙarin gabatar da wasu mutane domin matsayin jagoranci, majalisar ta tsaya a abin da ta tabbatar. Har sai daren 19 ga watan Ramadan, daren Lailatul-Qadr, inda wannan yardar Allah da “rubutaccen hukunci” ya sauka ga majalisar da kuma al’ummar Iran ta hannun Imamuz Zaman (AJ).
Godiya ga Kamfanin Dillancin Labaran Hauza
A ƙarshe, ina so in yi godiya ga ɗaya daga cikin ingantattun cibiyoyin yada labarai — Kamfanin Dillancin Labaran Hauza — wacce ke bayyana hakikanin al’amura tare da bin diddigin fayyace gaskiya. Wannan cibiyar, kamar yadda tsofaffi kan ce, tana “haske da bayyana tunani.” Ina roƙon Allah ya ba su karin nasara, iko da taimako. Sun kasance masu ƙwarewa a fannin aikin jarida, kuma insha’Allah a nan gaba za su sami nasarori mafi girma — musamman wajen haɗin kai da cibiyoyin ilimi na Shi’a da Sunna a sassa daban-daban, da kuma a harsuna daban-daban. A ganina, duniya yau ta koma duniyar kafofin yaɗa labarai, kuma ku kun yi matakai masu kyau; ina fata za ku ɗauki matakai mafi girma nan gaba.
Ra'ayinka